Babu Wani Mahaluki Da Zai Iya Kayar Da Shugaba Muhammad Buhari A Filin Zaɓe

233

Gwamnan jihar Kaduna Nasir el-Rufa’i ya ce ba a taɓa ɗan siyasa ko ma’aikacin gwamnati da talakawa suka yarda da shi a kasar nan kamar Shugaba Muhammadu Buhari.

Gwamnan ya ce ‘yan kasar nan sun san tarihin shugaban bai taba cin amana a ayyukan da ya gudanar ba a baya.

Ya ƙara da cewa babu wani dan siyasa a faɗin ƙasar nan da zai iya kayar da shugaba Buhari a fagen siyasa

Ya kuma soki tsohon Shugaba Olusegun Obasanjo, inda ya ce “idan aka ji Obasanjo na maganganu akwai abin da ya nema a gwamnati bai samu ba. Saboda haka ba don Allah yake yi ba,” in ji Gwamna el-Rufai.

Sai dai ya bayyana cewa har yanzu akwai abubuwan da ya kamata a kara gyarawa a gwamnatin Buhari.

Amma ba zai bayyana su ba, saboda a cewarsa ba ya ba da shawara a kafafen yada labarai. Ya ce idan zai ba shugaban shawara zai kebe ne da shi a fadarsa.

Har ila yau ya bayyana daukar Dokta Hadiza Balarabe a matsayin mataimakiyarsa a zaben 2019 a matsayin wani yunkuri na ci gaban jihar, ba wai don kawo rabuwar kai a bangaren addini ba.

A bangaren korar malamai ya bayyana cewa mafi yawancin malaman da aka korar a jihar “jahilai ne saboda bai kamata a ce suna aji suna koyarwa ba,” in ji ta.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan