Rundunar Yansandar Jihar Zamfara Ta Musanta Rahoton Saka Dokar Ta Baci

211

Rundunar Yansanda ta jihar Zamfara ta karyata rahoton gidan wani jarida da yace rundunar ta sa dokar hana fita a jihar biyo bayan yawan kashe-kashe da garkuwa da mutane domin biyan kudin fansa.

A wani hira na musamman da jaridar Daily Post a jihar Gusau, mai magana da yawun rundunar S.P. Muhammad Shehu yace mai rahoton bai fahimci rundunar Yansandan ba shi yasa ya yi rahoton ba dai-dai ba.

S.P. Muhammad yace , rundunar Yansanda ta hana baburan Acaba da Adaidaita sahu watau Keke-Napep zirga -zirga daga karfe shida na yamma zuwa bakwai na safe a kullum saboda sun gano yan-ta’addan na amfani da wadannan ababen hawan wajen kaddamar da mugun aikinsu.

Ya kara da cewa rundunar Yansanda bata sanya dokar hana zirga-zirga ba a jihar ta Zamfara ba, dan jaridar ne ya yi rahoton ba dai-dai ba.

A ranar Laraba da ta gabata ne, kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautun gargajiya ya yi taron ganawa da Sarakuna da shugabannin Fulani a garin Gusau, inda yace gwamnati tana kan bakanta na dokar hana zirga-zirga daga karfe bakwai na yamma zuwa bakwai na safe akan masu ababen hawa a jihar saboda rashin wadataccen tsaro amma rundunar yansanda bata ce komai ba akan maganar da ya yi.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan