Rikicin Zamfara: Babu Batun Tattaunawa da Yan Ta’adda Inji Kwamishinan Yansanda

150

Kwamishinan Yansandar Jihar Zamfara Mista Celestine Okoye ya ce jami’an tsaro ba zasu yi batun sasantawa da yan ta’addan da suka addabi mutane a jihar ba.

Mista Okoye ya bayyana matsayar na jami’an tsaro bayan kammala taro akan tsaron jihar Zamfara a Talatar-Mafara.

Ya kara da cewa babu batun tattaunawa ko sasantawaba tsakanin su da yan ta’addan saboda jami’an tsaro sun shirya tsaf domin fatattakarsu daga jihar.

Kwamishina Celestine ya ce aikin ta’addanci a jihar Zamfara ya zo karshe amma a yanzu ba zasu bayyana matakan da zasu bi ba wajen kawar da su.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan