An yi Artabu Tsakanin Ƴan Bindiga da Jama’ar Zamfara

197

Mutanen Badarawa Sun Yi Arangama Da Barayin Shanu Sun Dawo Da Nasara


Jama’ar garin Badarawa, sun yi arangamar fito-na-fito da wani gun-gun barayin shanu, a daren jiya.


Arangamar ta biyo bayan kokarin ‘yan ta’addan na afkawa garin.


Mutanen garin sun yi nasarar kashe barawo biyu. A daya bangaren, barayin sun kashe mutum daya cikin mutanen garin, sannan sun kore wasu dabbobi da ke kiwo a fadamar garin.


Garin Badarawa da ke karamar hukumar mulkin Shinkafi, na daga cikin garuruwan da ke fuskantar hare-haren ta’addanci.

Daga Abdurrahman Abubakar Sada


Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan