Ramadan: Ɗangote ya tallafa wa gajiyayyu a Enugu

168

Gidauniyar Dangote, DF ta tallafa wa mabuƙata Musulmi a jihar Enugu a wani shirinta na Ciyarwa na Watan Ramadan na 2019.


Kamfanin Dillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya ruwaito cewa an kayan tallafin ne ga mabuƙata da ba su gaza 500 a Abakaliki ranar Litinin.


Kayan tallafin sun haɗa da katan ɗin pasta 250, buhun gishiri mai nauyin kilogiram 1 guda 500, buhun sikari mai nauyin kilogiram 1 guda 500, buhun Samolina mai nauyin kilogiram 5 guda 500, da buhun alkama ma nauyin kilogiram 10 guda 250.


Ndagi Ahmed shi ne jami’in da ya duba yadda aka raba kayayyakin.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan