Buhari ya rantsar da Mohammed Tanko a matsayin Alƙalin Alƙalan Najeriya

125

Shugaba Muhammadu Buhari ya rantsar da Mai Shari’a Mohammed Tanko a matsayin tabbataccen Alƙalin Alƙalan Najeriya, CJN.

Mista Mohammed, wanda aka rantsar a Fadar Shugaban Ƙasa dake Abuja ranar Laraba ya zama Alƙalin Alƙalai na 18.

A makon da ya gabata ne Majalisar Dattijai ta tantance tare da amincewa da Mista Mohammed, wanda ya gaji tsohon Alƙalin Alƙalai, Walter Onnoghen.

Tun a watan Janairun bana ne ya zama Muƙaddashin Alƙalin Alƙalai.

Ya samu muƙamin CJN ne bayan Shugaba Buhari ya dakatar da Mista Onnoghen bisa zarginsa da ba dai-dai ba a wajen bayyana kadarorinsa.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan