A yau Juma’a 16 ga watan Augusta za a fara gasar Laliga ta kasar Andalos sabuwar kaka fil a leda ta 2019 zuwa 2020.
Ayau din dai masu rike da kambun gasar wato kungiyar kwallon kafa ta Barcelona zata kara da Athletico Bilbao.

Kungiyar kwallon kafan da tafi lashe gasar itace Real Madrid inda ta lashe gasar sau 33 inda Barcelona ta lashe kofin sau 26.
Shin ko yaya wannan kakar wasan ta bana zata kasance ganin cewa kowacce kungiyar kwallon kafa mai buga gasar Laliga tayi gyara?
Turawa Abokai