Alƙawura 10 Da Buhari Ya Ɗauka A Sabuwar Shekara 2020

242

Alƙawura 10 Da Buhari Ya Ɗauka A Sabuwar Shekara 2020

Shugaba ƙasa Muhammadu Buhari ya dauki wasu sababbin alkawurran da ya sha alwashin cikawa a cikin shekarar 2020.

Cikin jawabin da ya gabatar ranar Laraba a ranar 1 Janairu, 2020, Buhari ya yi dogon jawabin da ya tunatar da ‘yan Najeriya dajin da gwamnatin sa ta keto, wasu nasarori da aka samu da kuma kalubalen da ke Gavan gwamnatin sa.

  1. Zan gina titina 47 a fadin kasar nan, wadanda za a kammala aikin su tsakanin 2020 zuwa 2021.
  2. Zan gina manyan gadoji masu tarin yawa a kasar nan cikin 2020, ciki har da ci gaba da ginin Gadar Kogin Neja Sashe Na 2.
  3. Zan gina rukunin gidaje masu tarin yawa cikin 2020, har rukuni-rukuni 13.
  4. Zan kaddamar da gaggarimin Shirin Inganta Noman Karkara wanda za a yi a Kananan Hukumomi sama da 700. Shirin zai dauki shekara uku ana gudanar da shi domin ya kankama ka’in-da-na’in.
  5. Zan kaddamar da shirin samar wa makiyaya kadadar kiwo a Jihar Gombe, mai fadin hekta 200,000.
  6. Zan horas da ma’aikata 50,000 a cikin 2020 domin kara yawan wasu 7,000 da ake da su da suka samu horo.
  7. Nan da watanni uku zan fara aikin titin jirgin kasa daga Ibadan zuwa Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano.
  8. Zan bada dama masu jari su sa hannu wajen inganta samar da wutar lantarki, ta yadda za ta kara inganta sosai.
  9. Zan fara ginin Tashar Hasken Lantarki ta Mambilla nan da watanni uku.
  10. Zan samar wa mutane milyan 100 aiki, nan da shekaru 10.
Turawa Abokai

1 Sako

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan