Mininistan harkokin noma na ƙasa Muhammad Sabo Nanono ya ƙalubalanci gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi kan matsalar tsaro a Najeriya.
A wata zantawa da ministan yayi da sashen Hausa na Radio France International kan yadda matsalar tsaro ta shafi ɓangaren noma.
Ministan ya ce “magana ta Allah da Annabi ba gwamnatin tarayya ce ta ke da haƙƙin tsaron wannan abu kawai ba, gwamnatocin jihohi ƙananan hukumomi, in ka tafi ƙasa har Dagatai da masu unguwanni, ya aka yi suka sake suka bar wannan yanayi na tsaro ya zama abin da ya zama, amma kowa ya tashi sai ya ce gwamnatin tarayya”.
“Eh gwamnatin tarayya tana da haƙƙin ta tsare rayuwa na jama’a, amma ai su waɗannan da suke kusa da waɗannan mutanen su ya kamata tun da farko ma su fara maganar cewa muna ganin muna da matsala a kan waɗannan abubuwan”.
Sabo Nanono ya ƙara da cewa gwamnatin tarayya tana iya ka ƙoƙarinta wajen bunƙasa noma da samar da abinci a ƙasar nan.


- Ibrahim Little: Gogarman ɗan siyasar da ke motsa PDP da takarar Atiku Abubakar a Kano
- Gwamna Badaru Abubakar ya amince da Muhammad Hameem a matsayin sabon Sarkin Dutse
- Bayanan Ƙarya aka Bawa Shugaban Ƙasa kan Canjin Fasalin Kuɗi – Fadar Shugaban Ƙasa
- Yanzu na Fara Wasan Barkwanci, Martanin Daso ga Jama’a
- 2023: Abba Kabiru Yusuf ya ƙauracewa muhawarar da Media Trust ta shirya
Karuwar hare-hare da sauran aiyukan ta’addanci na zuwa ne a daidai lokacin da mahukuntan Najeriya ke ikirarin aniyar murkushe ‘yan bindiga dadi da sauran masu tayar da kayar baya.