Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kashe kudi fiye da Naira Miliyan Dari hudu da talatin kan gangamin yaki da cutar Polio a fadin jihar nan a wannan shekarar.
Kwamishina lafiya Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya bayyana hakan a yau yayin taron manema labarai kan shirye-shiryen fara yib allurar rigafin cutar a nan Kano.
Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ya ce za’a fara gangamin rigakafin vutar polio daga gobe 31 ga watan Oktoba zuwa 3 ga watan Nuwamba, inda za a kaddamar da shirin a karamar hukumar Garko.
- Yadda Obasanjo Ya Yi Aikin A Daidaita Sahu A Abekuta
- Ina fatan Fim ɗin Lulu da Andalu ya kere sa’a a wannan shekara ta 2022-Jarumi TY Shaban
- Sojan Gona: Kotu a Ilorin ta tura sojan ƙasar Amurka gidan yari
- Yaƙin Rasha Da Ukraine Zai Ci Gaba Da Haifar Da Tsadar Abinci A Afirka
- Hanyoyin da zaku bi domin sabunta katin zabenku
Kwamishin lafiyar ya kuma yabawa kokarin masu ruwa da tsaki a yakin da ake da cutar Polio tsawon shekaru goma wanda ya kai ga jihar ta kubuta daga cutar tsawon shekaru.
Idan za’a iya tunawa dai, a ranar 25 ga watan Agusta ne na shekarar 2020 a ka sanar da cewa yankin Afrika ya kubuta daga cutar bayan shafe shekaru hudu ba a samu dauke da cutar ba.