Bayan kiran ƙauracewa kayayyakin Faransa, musulmi a birnin Kano sun gudanar da zanga-zanga domin ci gaba da nuna fushi kan kalaman shugaban ƙasar Faransa da kuma ɓatanci ga Annabi Muhammad SAW.
Tun da farko masu zanga-zangar sun fara tattaki da misalin ƙarfe 12 na ranar Lahadi daga Unguwar Gwammaja a ƙaramar hukumar Dala.
Masu zanga-zangar a birnin Kano na dauke da kwalaye da aka yi rubutun Allah wadai da shugaban ƙasar Faransa.


- Ibrahim Little: Gogarman ɗan siyasar da ke motsa PDP da takarar Atiku Abubakar a Kano
- Gwamna Badaru Abubakar ya amince da Muhammad Hameem a matsayin sabon Sarkin Dutse
- Bayanan Ƙarya aka Bawa Shugaban Ƙasa kan Canjin Fasalin Kuɗi – Fadar Shugaban Ƙasa
- Yanzu na Fara Wasan Barkwanci, Martanin Daso ga Jama’a
- 2023: Abba Kabiru Yusuf ya ƙauracewa muhawarar da Media Trust ta shirya
Mukhtar Nalele wanda shi ne shugaban masu zanga – zangar ya bayyana cewa, ya zama wajibi su nuna fushi a kan kalaman ɓatanci da shugaban Faransa ke yiwa addinin musulunci.
Haka kuma Mukhtar Nalele ya buƙaci al’ummar musulmi da su ƙaurace wa sayen kayan da aka yi shi a ƙasar Faransa domin yin tir da abin da ke faruwa.
Kazalika ya yi kira ga dukkan musulmai da su zama tsintsiya madaurinki daya.
Wannan zanga zangar dai na zuwa ne a lokacin da shugaba Emmanuel Macron ya sha alwashin kiyaye abin da aka san Faransa da shi a matsayin ƴar ba ruwana da kowanne addini.