Gidan rediyon Vision FM da ke jihar Kano ya karrama shugaban hukumar yaki da rashawa da cin hanci ta jihar Kano, Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado da lambar yabo ta gwarzon yaƙi da zalunci da kuma cin hanci da rashawa.



Taron bikin karramawar ya gudana ne a harabar gidan rediyon na Vision FM da ke unguwar farm centre da ke birnin Kano.


Haka kuma taron ya samu halarcin fitattun mutane da jami’an gwamnati da ƴan siyasa da kuma malamai.

Turawa Abokai