A yau Lahadi Masarautar Argungun da ke jihar Kebbi a Najeriya ta naɗa ministan yaɗa labarai da al’adu na ƙasa Alhaji Lai Mohammed sarautar Kakakin Kebbi.
Nadin sarautar ya biyo bayan amincewa da majalisar masarautar ta Argungun karkashin mai martaba Sarkin Argungun Alhaji Sama’ila Mera.

Da yake jawabi a wajen taron, Sarkin na Argungun ya ce an ba wa ministan wannan sarautar ne saboda “jajircewa da ƙarfin hali wajen nuna hoton Najeriya a gida da waje ”.
Alhaji Sama’ila Mera ya ce masarautar ta karrama ministan da mukamin ne a matsayin nuna godiya ga kokarinsa na inganta bikin kamun kifi da al’adun Argungu don samun matsayin duniya.

Haka kuma Sarkin na Argungun ya kuma yaba wa tsoffin ministocin al’adu da yawon bude ido kan kokarin da suke yi na inganta bikin a kasa baki daya tun shekarar 1970.

Kuna iya bibiyarmu ta kafafen sada zumuntarmu a
Facebook
YouTube
Instagram
Telegram
Ko kuma ku aiko mana da gyara ko shawara ta adireshinmu na email – Labarai24@yahoo.com
Ku shiga group dinmu don samun labaru kullum 👉 WhatsApp
[…] Roll-Royce Phantom wadda darajar ta ke kaiwa daga Dalar Amurka $455,000 zuwa $535,000, idan aka yi lissafinta a Naira za ta kai Naira miliyan N187mn zuwa N219.8mn (a farashin Dala na Banki). ku karanta:Masarautar Argungun ta naɗa Lai Mohammed kakakin Kebbi […]