Kanywood: Jaruma Rahama Sadau ta saje da ‘Indiyawa’

995

Fitacciyar jarumar fina-finan Kannywood Rahama Sadau na cigaba da wallafa hotunan ta tare da wasu jaruman fina – finai a masana’antar Bollywood da ke ƙasar India a shafinta na Instagram.

Jaruma Rahama Sadau da sauran jaruman Bollywood a ƙasar Indiya

Tun a cikin farkon watan nan na Satumba masu amfani da shafukan sada zumunta musamman waɗanda su ke bin diddigin rayuwar fitacciyar tauraruwar Kannywood ɗin su ka fara wallafa hotunan ta a ƙasar Indiya tare da bayyana ra’ayoyi mabambanta bayan da ta isa ƙasar.

Jarumar Kannywood ɗin dai ta isa ƙasar ne domin fara fitowa a wani sabon fim na Bollywood mai suna Khuda Haafiz.

Jaruma Rahama Sadau

Sai dai wani abu da ke baiwa al’umma mamaki shi ne yadda jarumar ta rikide ta koma tamkar Ba – Indiya domin a duk hotunan ta da ta wallafa sun yi matuƙar sajewa da sauran jaruman na Bollywood.

Idan za a iya tunawa dai a cikin shekarar 2015 Rahma Sadau ta fara fitowa a fina-finan kudancin Najeriya da aka fi sani Nollywood, inda ta fito a cikin wani shirin fim mai suna ‘The Light Will Come’.

Kuna iya bibiyarmu ta kafafen sada zumuntarmu a

Facebook
YouTube
Instagram
Telegram
Ko kuma ku aiko mana da gyara ko shawara ta adireshinmu na email – Labarai24@yahoo.com

Ku shiga group dinmu don samun labaru kullum 👉 WhatsApp

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan