Atiku Abubakar ya yi ganawar sirri da Sule Lamido da Gwamnan Bauchi Bala Muhammad

723

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma ɗan takarar shugabancin kasar a zaɓen shekarar 2019 Alhaji Atiku Abubakar ya yi wata ganawar sirri da tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido a gidansa da ke birnin tarayya Abuja.

Atiku Abubakar ya wallafa hotunan ganawar da ya yi da Sule Lamido a shafinsa na facebook a jiya a Juma’a.

Lokacin da Sule Lamido ya ziyarci Atiku Abubakar

Awanni kaɗan da fitar da hotunan ganawar da Atikun ya yi da Sule Lamido sai ga shi kuma Gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad shi ma ya ziyarci Atiku Abubakar.

Atiku Abubakar da Gwamnan jihar Bauchi Bala Abdulkadir Muhammad

Wannan ganawar dai na zuwa ne mako ɗaya da kwamitin zartarwar jam’iyyar PDP na kasa ya amince da matakin da kwamitin raba mukamai a jam’iyyar ya yi na keɓewa yankin arewacin ƙasar nan kujerar shugaban jam’iyyar al’amarin da ya haifar da tada jijiyoyin wuya.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan