Najeriya Za Ta Fara Ƙera Makamai Don Sauƙaƙa Yaƙi Da Ta’addanci— Buhari

336

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari ya bayyana cewa nan gaba kaɗan Najeriya za ta fara ƙera makamai domin sauƙaƙe yaƙi da matsalolin tsaro da take fama da su, a cewar wani rahoto na BBC Hausa.

Shugaba Buhari ya bayyana hakan ne ranar Litinin yayin taron da yake jagoranta na kwana biyu a Fadar Shugaban Ƙasa kan ayyukan da gwamnatinsa ke gudanarwa a ma’aikatu daban-daban, kamar yadda rahoton na BBC Hausa ya ce.

Shugaban Najeriyar ya ce tuni aka bai wa Ma’aikatar Tsaro umarnin ƙirƙiro wata masana’anta domin ƙera makamai a cikin gida da zummar biya wa rundunar sojan ƙasar buƙatunta.

Ya ƙara da cewa samar da masana’antar makaman a Najeriya zai bayar da damar rage dogaro da ƙasar ke yi kan ƙasashen waje.

Za a ƙaddamar da shirin ne a ƙarƙashin Sashen Masana’antu na Rundunar Sojan Najeriya mai laƙabin Defence Industries Corporation of Nigeria (DICON), a cewarsa.

Ya zuwa yanzu Najeriya ta yi nasarar ƙera jiragen ruwa na soja da wasu ƙananan tankokin yaƙi waɗanda shugaban ya ƙaddamar a ƙarshen 2020.

A Yulin da ya gabata ne kuma Najeriya ta karɓi jiragen yaƙi da ta sayo daga Amurka na A-29 Super Tucano, waɗanda Buhari ya ce “ana amfani da su wajen bayar da horo da kai farmaki da tattara bayanai ga dakarun Najeriya”.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan