Gwamnatin Tarayya ta Ware Biliyan 104 dan Sayen Janareta a Lokacin da ‘yan Ƙasar ke Tuni kan ina Dokar Hana Shigo da Janareta ta Tsaya?

385

Tuni dai tunanin ‘yan Nijeriya ke ci gaba da hasashen tare da kokwanton cewa yaushe Nijeriya za ta kawo ƙarshen matsalar harsken wutar lantarki a dai dai lokacin da ma’aikatun gwamnatin tarayya daban-daban a shekarar 2022 su ka ware biliyan 104 dan sayen Janareta da zai basu wuta da zuba masa mai a shekarar 2022.

A dadin kuɗaɗen da aka ƙiyasta sun zarta kuɗin shigar jihohi 24 a ƙasar.

Hakan dai na ƙunshene a cikin bayanan dake tattare a kasafin kuɗin Nijeriya na shekarar 2022 wanda majalisa ke tantan cewa zuwa yanzu.

Wasu Janareta agun gyara

Lamarin dai na ci gaba da tabbatar da taɓarɓarewar harkar samar da wutan lantarki a Nijeriya duk da maƙudan kuɗaɗen da ake zubawa wannan sashi da ya kai ga cefanar da wasu sassansu a hannun ‘yan kasuwa.

Wanda ko a shekara ta 2020 a ƙoƙarin gwamnatin na daƙile shigo da Janareta, ta sanya gabatar da ƙudirin da zai hana shigo da Janareta daga ƙasashen waje. Dokar da a lokacin ake hasashen zata taimaka wajen bunƙasa harkar wutar lantarki a Nijeriyar.

Har wa yau dai a lokacin ta kaiga hatta majalisar dokokin Najeriya na kasafta maƙuddan kuɗaɗe wajen shigo da Janaraito a ƙasar, amma har zuwa yanzu wannan doka bata kai ga cimma gaci ba.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan