Za Mu Share Wa Talakawa Hawaye Duk Da Matsin Tattalin Arziƙi— Gwamnatin Najeriya

595

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta lashi takobin cewa za ta share wa talakawa hawaye duk da matsin tattalin arziki da ake fuskanta a ƙasar.

Ministar Jin Ƙan Al’umma, Kare Afkuwar Annoba da Walwalar Jama’a, Sadiya Umar Farouq ce ta bayyana haka a yayin ƙaddamar da wani shiri mai suna Mobile Money Agents Training Programme ranar Litinin a Kano.

Ta ce haka ne ya sa ta ɓullo da Shirin Walwalar Jama’a na NSIP a matsayin wani mataki da za a rage wa marasa galihu raɗadin talauci.

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari

Sadiya ta ce a shekaru biyar da suka gabata, fiye da iyalai miliyan 12 suka amfana da shirin na NSIP a faɗin ƙasar nan.

“Duba da sauyin rayuwa da waɗanda suka amfana da NSIP suka samu, Shugaba Buhari ya amince a ƙara wa’adin shirin don a tabbatar da cewa kowa an fitar da kowa daga talauci”, in ji ta.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan