Zulum Zai Fara Biyan Malaman Makaranta Mafi Ƙarancin Albashi Na N30,000

314

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya yi alƙawarin cewa zai fara biyan naira N30,000 ga malaman makaranta a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Hakan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Maitaimakin Gwamnan Kan Kafafen Yaɗa Labarai, Isa Gusau ya fitar ranar Talata.

A yanzu haka wasu malaman a jihar Borno albashinsu bai gaza naira 11,000 ba sakamakon ayyukan malaman bogi, kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Daga Hagu, Gwamna Zulum Yana Tattaunawa Da Wani Ɗan Jarida

“Ɗaya daga cikin manyan matsalolin harkar ilimin firamare a Borno a yau ita ce kula da walwalar malamai. Abin takaici ne a ce har yanzu akwai masu karbar naira N13,000 ko 11,000 a matsayin albashi.

“Ina so na tabbatar da cewa duk da ƙalubalen da ake fama da shi na tattalin arziki, muna aiki don ganin cewa kowane malami da ya cancanta a Borno yana karbar naira N30,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi”, in ji Gwamna Zulum kamar yadda BBC Hausa ta rawaito.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan