Halifan Tijjaniyya, Sanusi II Zai Fara Karatun Digiri Na Uku A Landan

244

Tsohon Sarkin Kano, kuma Halifan Tijjaniyya a Najeriya, Muhammad Sanusi II, zai fara karatun digiri na uku a Jami’ar Landan, Birtaniya.

Tsohon Sarki Sanusi, wanda ya bayyana haka ga editan jaridar Intanet, PREMIUM TIMES ranar Litinin, ya ce kwanan nan ya koma Landan don yin digirin na uku.

A farkon 2019, Sanusi II ya samu kyautar digirin girmamawa a Fannin Kuɗi a wata makaranta mai suna School of Oriental and African Studies, SOAS, Jami’ar Landan.

A 1997 ne Sanusi II ya kammala digirin farko a Nazarin Addinin Musulunci a Jami’ar Ƙasa da Ƙasa ta Afirka, Khartoum, Sudan.

Haka kuma, a 1981, Sanusi II ya yi wani digirin na farko a Tattalin Arziƙi a Jami’ar Ahmadu Bello, Zariya.

Jami’ar Oxford, Landan, ta ba Sanusi II matsayin malamai mai ziyara.

Tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, CBN, wanda kwaɗayinsa a ilimi ba zai misaltu ba, a iya cewa yana ɗaya daga cikin ‘yan Najeriya mafiya ilimi da ya taɓa zama Sarki.

A halin yanzu zai haɗa Sanusi II zai riƙa tauna raura biyu ne; kasancewa malami mai ziyara a Jami’ar Oxford, kuma ɗalibi mai karatun digiri na uku a Jami’ar Landan.

Wata biyar bayan an cire shi daga Sarkin Kano, sai Jami’ar Oxford ta amince da buƙatar Sanusi II ta zama malami mai ziyara.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan