Gwamantin tarayya za ta ƙara farashin tikitin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna

175

Ministan sufuri na Najeriya Mu’azu Sambo ya ce za a yi ƙarin kuɗin tikitin jirgin ƙasan da ke zirga-zirga tsakanin babban birnin ƙasar Abuja, da kuma Kaduna mai maƙwaftaka.

Ministan ya faɗi hakan ne a lokacin da ya gana da manema labaru, sa’ilin da aka yi gwajin jirgin a shirye-shiryen da ake yi na dawo da sufurin.

Ya ce za a yi ƙarin ne bisa dogaro da sauyin da aka samu na tattalin arziƙi.

Ministan ya ce ma’aikatar sufuri na tattaunawa da hukumar lura da jiragen ƙasa ta Najeriya domin ganin ko za a yi ƙarin farashin ne nan take ko kuma za a jinkirta.

Ya ce “kowa ya san cewa farashi ya tashi, hatta farashin tikitin jiragen sama ya tashi, me zai sa mutane su yi surutu idan an ƙara farashin tikitin jirgin ƙasa?”

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan