Buhari Ya Yi Wa Wamakko Ta’aziyyar Rasuwar Matarsa

118

Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, ya yi wa tsohon Gwamnan jihar Sakkwato, Aliyu Magatakarda Wamakko, ta’aziya, bisa rasuwar matarsa.

Shugaba Buhari ya bayyana saƙon ta’aziyyarsa ne a cikin wani saƙo da Mai Magana da Yawunsa, Garba Shehu, ya sanya wa hannu.

A cewar Shugaba Buhari, labarin rasuwar mai ɗakin Wamakko ya kaɗa masa zuciya.

“Rashin matar da ta kasance wani muhimmin ɓangare a rayuwark, uwar ‘ya’yanka, raɗaɗi ne mai wahalar riƙewa”, in ji sanarwar.’

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan