Tsohon dan wasan Najeriya ya koma yin gadi

302

Tsohon Dan Wasan Flying Eagles, Bello Mohammed ya koma sana’arsa gadi.

Bello Mohammed Ya buga wasa a Flying Eagles ta Najeriya a tsakanin shekarar 1999-2000, inda ake yi masa lakabi da ‘Bello Sudan’ saboda kuzarinsa da karfinsa.

Dan wasan wanda a kodayaushe a shirye yake ya ba da ransa ga kasarsa, majiyoyi sun tabbatar da cewa yanzu shi jami’in gadi ne a wata cibiya a Abuja.

Bello ya buga wasa a El-Kanemi Warriors, Yobe Dessert Stars, da Zamfara United.

YA buga wasa a Najeriya, tareda Taurarin yan wasa irin su: Isa Hudu, marigayi Justice Christopher, Christian Obodo, Kelechi Okoye, Olaniyi Olayinka, Austin Ejide, Aniekan Enyeama, Dele Aiyenugba, Ajibade Omolade, Onyebuchi Chukwumah da dai sauransu.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan