Hukumar Zabe ta Samar Da Mafita Ga Rikicin Jihar Kano

196
Akwatin zaɓe

Hukumar zabe mai zaman kanta ta Kasa INEC, ta bayyanawa manema labarai cewa ta samu mafita ga matsalar da ta dakatar da tattara sakamakon zaben gwamnan jihar Kano.

Jami’in tattara bayanai na jihar Kano, Farfesa Bello Shehu ne ya bayyana hakan a yau litinin.

A daren jiya ne hatsaniya ta barke a karamar hukumar Nasarawa a yayin da ake tattara kuri’u wanda shine karamar hukumar da ta karshe don kuri’u su kammala a bayyana sakamakon zaben gwamna.

A lokacin hatsaniyar ne, aka yayyaga takardun da ke dauke da takardun da suke dauke da sakamakon kuri’un.

Yanzu haka, hukumar INEC tace, zata yi amfani da sakamakon da ke cikin na’urar tattara bayanai domin kara kirga kuri’un karamar hukumar Nasara saboda a samu a kammala tare da bayyana sakamakon

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan