Zan Jagoranci Fafutukar Soke Hukuncin Kisa A Duniya— Shugaban Faransa

416

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron, ya ce zai jagoranci wani kamfe don soke hukuncin kisa a faɗin duniya, a daidai lokacin da ake cika shekara 40 da soke hukuncin a Faransa, a cewar wani rahoto na BBC Hausa.

Mista Macron ya ce a hukumance aƙalla mutum 483 aka yanke wa hukuncin kisa a faɗin duniya bara – kuma mafi yawansu gwamnatocin da ke aiki da demokuraɗiyya ne suka yanke hukuncin, in ji BBC Hausa.

Ya ce a wani ɓangare na shugabancin Tarayyar Turai da Faransa za ta yi a shekara mai zuwa, ƙasar za ta shirya wani taro da manyan jami’an gwamnati za su halarta, wanda zai taimaka wurin shawo kan shugabannin ƙasashe su soke hukuncin.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan