2023: Ko Badaru Abubakar zai zama ɗan takarar shugabancin Najeriya a APC?

370

A daidai lokacin da ƴan siyasa a jam’iyyar APC musamman waɗanda su ka fito daga yankin kudancin Najeriya ke cigaba da bayyana aniyarsu ta tsayawa takarar kujerar shugaban ƙasar a zaɓen 2023.

Sai ga shi Gwamnan jihar Jigawa, Muhammad Badaru Abubakar ya garzaya sakatariyar jam’iyyar a jiya Laraba, inda ya yanki fom ɗin neman APC ɗin ta sahale masa takarar shugabancin Najeriya a kakar zaɓe mai zuwa.

Gwamna Badaru wanda ya fito shiyya ɗaya da shugaba Muhammadu Buhari, ya sayi fom ɗin ne a dai-dai lokacin da manyan jam’iyyun Najeriya guda biyu PDP da APC su ke muhawara akan wacce shiyya ya kamata su kai takarar shugabancin ƙasar a 2023.

Haka kuma Gwamnan ya yi wata ganawa ta musamman da Shugaban jam’iyyar na ƙasa Sanata Abdullahi Adamu a gidansa da ke Abuja jim kaɗan bayan bayyana kudirin na sa.

Gwamna Muhammad Badaru Abubakar da shugaban jam’iyyar APC Abdullahi Adamu

Sai dai wata majiya daga fadar gwamnatin Jigawa da ta buƙaci a sakaye sunanta ta shaidawa Labarai24 cewa umarni ne daga fadar shugaban ƙasa a ka baiwa gwamnan dan neman shugabancin a jam’iyyar ta APC.

Duk abin da ka ga mun yi akwai lissafi, domin shi mai girma Gwamna ba zai taɓa yin abu babu lissafi”.

Kudurin na Gwamna Badaru na zuwa a lokacin da ake raɗe – raɗin akan jam’iyyar ta APC za ta sake dawo da takara shiyyar Arewacin Najeriya.

Haka kuma ana ganin Gwamna Muhammad Badaru Abubakar na da tasiri sosai a gurin shugaba Muhammadu Buhari da wasu masu faɗa a ji a cikin jam’iyyar APC.

Turawa Abokai

RUBUTA AMSA

Rubuta ra'ayinka
Rubuta Sunanka a nan